KannywoodLabaran duniya

Menene Hukuncin fitar da maniyya da Gangan a azumi ~ Malam Aminu Daurawa 

Menene Hukuncin fitar da maniyya da Gangan a azumi ~ Malam Aminu Daurawa

Wani Bawan Allah ya aiko wa Shiekh Aminu Ibrahim Daurawa tambaya, inda ya nemi fatawa a kan zubar da maniyyi a lokacin da mutum yake azumi.

Wannan mutum ya bayyana cewa ya na cikin yin waya da budurwarsa a wayar salula, sai ya ji maniyyi ya fito daga gabansa, alhali azumi ya na bakinsa. Kafin ya amsa tambayar, babban malamin na musulunci, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya ja-kunne a kan yin waya irin wannan a lokacin da ake azumi.

GADAI BIDIYON

Aminu Ibrahim Daurawa ya nakalto fatawar babban malamin fikihu nan, Ibn Abi Zayd Al-Qayrawani, wanda ya ce irin azumin wannan Bawan Allah ya karye. Sheikh Al-Qayrawani a littafinsa na Risala, ya ce wanda ya zubar da maziyyi da gangan a sanadiyyar sha’awa zai kama baki, sai ya rama azumi daya daga baya.

Haka zalika a fatawar bajimin malamin, duk wanda ya kai har ga zubar da maniyyi a lokacin azumi, sai ya yi kaffara; zai yi azumi 61 bayan watan na Ramadan.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Tallafin Ramadan N75,000 Daga Gwamnati

X
KALLI BIDIYON ANAN